An Kama Wani Katon Gardi Mai Shigar Mata Yana Shiga Makarantar Yan Mata Domin Ya Lallatse Su

An Kama Wani Katon Gardi Mai Shigar Mata Yana Shiga Makarantar Yan Mata Domin Ya Lallatse Su

Ga Bidiyon mutumcin

MUSULUNCI SHINE ADDININ DA YA DAUKAKA DARAJAR MACE

Kafin karni na 17 yahudu da nasara ba su dauki mace a matsayin halittar mutane ba, don haka ba su dauketa da daraja ba, sun bautar da mata, sun wulakanta su

Shiyasa manyan sarakunan Rumawa suke shirya wata irin gasa a wancan lokacin, suna sa a tara mata tsirara su zabi na zaba, shine abinda aka sani a yau “zaben sarauniyar kyawawa”

A Kasar Ingila har wajejen shekarun 70s ba su dena banbance tsakanin albashin mace da na miji ba, sun daukaka darajar albashin maza akan na mata, saboda yadda suka taso suka ga kakanninsu sunayi akan rashin daraja ‘ya mace

Turawan da wawayen Musulmai ‘yan boko aqeedah suke kwaikwayonsu a yau, abinda suka dauki mace itace wata haja da za’a kwanta a ji dadi da ita, sannan ayi talle da ita, sannan a jefa sharri da tarko da ita

Akwai wani bature tsohon mawaki ‘dan Amurka na manta sunansa, shi cewa yayi da zai samu dama da ya kwanta da matan duniya gaba daya, saboda yadda ba su dauki mata da daraja ba, yau su kwanta da wannan su jefar, gobe su kwanta da wancan, haka suke rayuwar kamar garken awaki

Salahudden yace, idan ana so a ruguza kasa cikin sauki ba tare da yaki na makami ba, hanyar shine barin mata suyi yawo tsirara tare da yaduwar zinace-zinace

Don haka duk lokacin da aka fara kiran mata su fita babu hijabi makirci ne, halaka mu ake so ayi, ance farkon fitinar da ta fadawa yahudawa ta afka musu ne ta sanadin mata

See also  Sati Biyu Dayin Aure Amarya Ta Fara Korafi Mijinta Baya Gamsar Da Ita A Kwanciyar Jima’i

Da jimawa, akwai manyan rikakkun ‘yan boko aqeedah da na sani a wannan dandali na facebook wadanda suke bada fatawar mata su cire hijabin su, suyi hoto babu hijabi su yada a media ba laifi bane, amma ban taba ganin daya daga cikin ‘yan boko aqeedar ya saka hoton matarshi ko ‘yarshi babu hijabi ba, da hijabin ma basu taba sawa ba

Sun killace matansu a gida, sun boye su don su kare mutuncinsu, sunzo suna kokarin halakar da matansu wasu da ‘ya’yan wasu, suna kaisu ga halaka da lalacewa, wannan tsananin mugunta ne da zalunci da cin amana, hakika babu wani mutumin kirki da zai ji dadi ana tallata matarsa ko ‘yarsa babu hijabi babu sutura na mutunci

Na san halin da mata suke fuskanta a kafofin sada zumunta saboda harin da mazinata suke kai musu, akwai matan da na san kyakkyawan niyya yake kawo su kafofin sada zumunta, don su boye kansu sai su bude account da sunan ‘ya’yan su maza ko kannensu maza, to ina kuwa ga wadanda suke bude account da sunansu na mata suna yada hotunansu babu hijabi? Allah ne kadai Ya san adadin lalatattun maza da suke kaddamar musu da mummunan hari

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *