May 19, 2024

Rahotanni sun bayyana cewa, motar dake daukowa mai tayi, hatsari sakamakon rashin birki, dake jikin babbar motar inda ta fada kan gadar kogin jihar adamawa kafin ta fashe.

Wani mutum ya shaida mana da cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 4:30 na yammacin ranar Lahadi, wanda yayi daidai da wannan wata da muke ciki na Satumber.

Mutumin ya bayyana cewa wannan shine babban bala’i na biyu daya kara afkuwa a yankin cikin wannan watan, sakamakon rashin kyakkyawar hanya dake tsakanin jihar kogi da kuma hanyar da za’a shigo arewaci.

Mutane da yawa daga cikin wadanda aka murkushe su, yayin da wannan lamari ya faru a lokacin sassan jikinsu sun tarwatse tare da kayayyakin dake hannun mutanan da lamarin ya aukawa lokacin.

Wasu daga cikin ‘yan uwan marigayan sun, bayyana mana cewa’ wannan wani lamari ne daya faru da ‘yan uwan nasu wanda kaddarace tana kan kowani bawa matukar yana rayuwa a duniya

Bawa zai ta ganin abubuwa da dama babu abinda zamuce face allah yayi musu rahama mu kuma idan tamu tazo allah yasa mu cika da imani cewar ‘yan uwan marigayan da wannan lamari ya faru dasu.

Kuci gaba da kasancewa da shafin ku, mai albarka Janzakitv, domin samun labaran duniya baki daya mungode masoyan mu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *