May 15, 2024

Assalamu alaikum barkan ku da kasancewa damu cikin wani sabon labari daya riske mu, a halin yanzu na wani rikekken mai garkuwa da mutane.

Sabon labari daga gidan jaridar rariya na wani crister, mai suna John Paul wanda ya kasance haifaffen dan asalin jihar taraba ne mazaunin jihar Lagos dake Nigeria.

John ya kasance mutum mai kamala a idon mutane sannan ya kasance mutumin dake baiwa mazauna unguwar da yake da zama shawara musamman matasa dangane da basu shawarar cewa’ yakamata su nemi na kansu.

Haka zalika ya kara dacewa neman halak nada matukar wahala yayin da yake bayyana hukumar ‘Yan sandan cewa yana baiwa matasan shawara saboda suyi kokarin neman na kansu cewar mutumin john.

Ashe John din, ya kasance bashi da aikin daya wuce garkuwa da mutane musamman hanyar Kaduna Abuja da sauran jihohi kamar irin su, katsina da kuma zamfara domin anan yafi samun kudaden shi.

Yanzu haka hukumar ‘yan sanda tana tsare dashi domin gudanar da bincike na gaskiya akan wannan lamari daya faru na kama mai garkuwa da mutanan wato John Paul mazaunin jihar Lagos.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *